1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAfirka

Yan sanda sun 'yanto wadanda aka sace

Ramatu Garba Baba
December 15, 2020

An kubutar da Indiyawan nan da wasu 'yan bindiga suka yi garkuwa da su a birnin Ibadan na jihar Oyo da ke Kudancin Najeriya. A ranar Larabar da ta gabata aka sace su kafin an 'yanto su a wannan Talata.

Symbolbild | Nigeria | SWAT
Hoto: AFP/Y. Chiba

Yan sanda a Najeriya sun ce sun yi nasarar 'yanto Indiyawan nan biyu da aka yi garkuwa da su a yankin Kudancin kasar a makon jiya. Wani mai magana da yawun rundunar sojin yankin Olugbenga Fadeyi, ya ce an yi musayar wuta a tsakanin 'yan bindiga da jami'an tsaro inda har soja guda ya ji rauni a lokacin da aka yi kokarin 'yanto Indiyawan. Ya ce an gano gawarwakin wasu mutane biyu a cikin dajin bayan da kura ta lafa amma ba tare da yayi karin bayani kan asalinsu ba.

An kama sune a birnin Ibadan a ranar Larabar da ta gabata. Daruruwan Indiyawa na ci gaba da rayuwa a Kudancin Najeriya duk da hadarin fadawa hannun 'yan bindiga da ke kama jama'a musanman 'yan kasashen waje suna neman kudin fansa. A Arewacin Najeriya kuwa, iyaye na cikin zulumi bayan garkuwa da aka yi da 'ya'yansu daga makarantar kwanan nan da ke Kankara a jihar Katsina. Kawo yanzu babu labari a game da halin da suke ciki, face ikirarin Kungiyar Boko Haram na cewa ita tayi garkuwa da daliban su sama da dari uku.