1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Ana zabe a inda ba a yi ba jiya

Ahmed SalisuMarch 29, 2015

Jama'a sun cigaba da kada kuri'unsu a yankunan da ba a samu kada kuri'a ba a ranar Asabar. Mazabu kimanin 300 ne dai aka gudanar da zabukan a ranar Lahadi.

Wahl in Nigeria Wählerinnen in Jigawa
Hoto: DW/Z.Rabo

Labaran da ke shigo mana daga Kano na cewar ana yin zabe a wasu mazabu da ba kai ga yin zaben na shugaban kasa da na 'yan majalisu ba a jiya. Wakilinmu Nasir Salisu Zango ya ce zaben na gudana ba tare da an fuskanci wani kalubale ba. Nasiru din ya ce can a ofishin hukumar zaben mai zaman kanta da ke Kano din ana cigaba da tattara sakamako na zaben kafin daga bisani a kai ga bayyana abinda kowanne dan takara ya samu.

Wakilinmu da ke Abuja kuwa Uwais Abubakar Idris ya ce a Abuja ma zaben na gudan ba tare da fuskantar matsaloli ba sai dai ya ce a wasu mazabun ba a yin amfani da na'urar nan ta tantance mutum wato Card Reader. Can ma a arewa maso gabashin Najeriya zaben na cigaba da gudana ba tare wani korafi ba a wuraren da ake gudanarwa.

A kudu masu yammacin kasar kuwa kusan a iya cewa an kammala zaben ma don yanzu haka an yi nisa wajen tattara sakamakon. Masu aiko da rahotanni suka ce sakamakon ya fita a kananan hukumomi da dama kuma ma tuni har an fara mika su ga zauren tattara sakamako na wasu jihohin yankin.

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW