1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Fatan 'yan Najeriya a sabuwar shekarar 2022

January 1, 2022

'Yan Najeriya na fatan samun sauyi na siyasa da tattalin arziki bayan irin wahalhalun da kasar ta yi fama da su na matsalar tattalin arziki da rashin tsaro da kuma batun 'yan aware na Biafra.

BG Silvester New York
Hoto: Seth Wenig/AP/dpa/picture alliance

Najeriyar da ta share dari na shekaru cikin batu na hadin kai dai na tangal-tangal tun da safiya ta sake sabuwar darin cikin tafiyar mai tsidau da kaya. Duk da cewar sabuwar awaren na dada kamari ne a lokaci na neman mulki a kasar, ra'ayi cikin kasar dai  yana rabe bisa sahihancin neman warewar da ta faro  jim kadan bayan zabe na 2015. Abdul Aziz Sulaiman dai na zaman kakaki na gamin gambiza ta matasan arewacin kasar da ke fadin warewar ce alheri ga makomar yankin nasu. ''Araba kowa ya kama hanya ta garinsu ko kuma a fake da rabawar da nufin cika buri na siyasa dai, in har arewacin tarrayar Najeriyar na fadin kowa ya tafi gida, ga masu fafutukar Biafran dai rashin adalci na kasar ne ke dada kai su zuwa bango a fadar Nnameker Ejiofor da ke zaman daya a cikin lauyoyin jagoran Biafran Nmandi Kanu.. ''Abun bakin ciki ne ace har yanzu a karni na 21, Najeriya  na makance ga adalci, har yanzu na makance ga yakamata, har yanzu na makance ga amintaccen tsari na kasa da kasa. IPOB dai kungiya ce mai neman zama na lafiya, dake rajin  yanci na cin gashin kai, da ke neman 'yancin cire kansu daga sarkar son zuciyar da ta mamaye wannan gwamnati. Abun da kawai suke nema ke nan adalci.”Zabukan da ke karatowar dai daga dukkan alamu na zaman zakaran gwajin dafi na makomar tarrayar Najeriya, kasa mafi girma a nahiyar Afrika ga batun yawan al'umma da tattali na arziki. 'Yan Najeriyar dai na fatan a wannan sabuwar shekara ta 2022 za a samu sauyi na tafiyar al'amura cikin kwanciyar hankali domin samun ci gaba mai dorewa.


 

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani