Bayan shafe shekaru 32, gwamnatin Tarayyar Najeriya ta ayyana aniyarta ta sake komawa yankin Ogoni mai arzikin man fetur
Aikin haka da tace man fetur, na taka rawa wajen gurbata muhalliHoto: Construction Photography/Photoshot/picture alliance
Talla
Aikin hakar man fetur a yankin na Ogoni dai, wamnatin ya dakata tun a shekara ta 1993. Kimanin gangar danyen mai dubu 28 yankin na Ogoni ke samarwa, kafin wani rikici tsakanin kamfanin mai na Shell da mazauna yankin ya tilasta tsai da aikin hakar man.
Ogoni na zaman daya daga cikin na kan gaba, a yankunan da ke samar da babbar hajar da kasar ta dauki lokaci tana kallo da idanun kima. Abujar dai na kallon man na Ogoni da fatan cike gibin gangar mai miliyan biyu, abin da kasar take da fatan ta haka kullum.
Kuma wani kokarin sulhunta tsakanin dattawan na Ogoni da gwamnatin kasar, ya kare da hukuncin sake komawa yankin da nufin ci gaba a cikin aikin da ke da fatan sake dora man na kan gaba cikin kudin shigar 'yan mulki.
Hakuri da manta baya
Aikin tsaftace yankin Ogoni na Najeriya
03:22
This browser does not support the video element.
Abun kuma da ya burge shugaban kasar da ke neman hanyar tara karin kudin shiga, ya kuma bai wa wasu dattawan na Ogoni hudu lambobin girma."Ina rokon al'ummar Ogoni a daukacin garuruwan yankin da su manta da banbamcin da ke a tsakaninsu, su dora mummunan tarihinsu a bayansu su ci gaba a matsayin al'umma daya da ke da hadin kai....." A cewar shugaban Najeriyar Bola Ahmed Tinubu.
Koma ya zuwa yaushe Abujar ke shirin ta kai cikin sabon tarihin na Ogoni dai, har ya zuwa yanzu tana gwa-gwa-gwa da wani shirin yasar dagwalon man fetur da kamfanin Shell na hakar mai ya bari a cikin yankin.
Sama da murabba'in kilomita 1000 na gurbataccen man ne dai, ya lalata wasu kauyuka 261 a cikin yankin. Farfesa Don Baridam dai shi ne shugaban wani kwamitin da ya jagoranci kokarin sulhunta tsakanin juna, kuma ya ce: "Batun muhalli a yankin na zaman na kan gaba, a kokarin sabon sulhun da ma sake fara aikin na hakar mai a cikin yankin....."
Kalubalen muhalli
Yankin Ogoni - Matsalar malalar mai a kullum
Malalar mai a Ogoni da ke a yankin Niger Delta mai arzikin man fetir a Tarayyar Najeriya, ta shafi sana'ar kamun kifi da noma a yankin.
Hoto: Katrin Gänsler
Sana'ar kamun kifi ta lalace
A da ƙauyen Bodo dake yankin Niger Delta ya rayu da sana'ar kamun kifi. Amma tun a shekarun 2008 da 2009 man fetir daga bututun mai na kamfanin Shell da ya ratsa cikin ƙauyen, ya fara malala, tarun masunya suka zama wayam. Duk wanda ke son ya rayu da sana'ar kamun kifi yanzu dole ya shiga teku, yayi aiki mai cin lokaci mai tsawo da kuma maƙudan kuɗaɗe.
Hoto: Katrin Gänsler
Dogaro da ruwa
Sai dai ba a Bodo ne kaɗai ba, a ilahirin yankin Niger Delta da ke kudu maso gabacin Najeriya, man fetir ya gurɓata musu ruwa, abin da ya zama babbar matsala. Al'ummar yankin na rayuwa a kan ruwa, da kuma rayuwan suke tafiyar da harkokinsu na yau da kullum. Har yanzu da kwale-kwale ake iya zuwa ƙauyuka da dama.
Hoto: Katrin Gänsler
Gurɓataccen mai a ko-ina
Hukumar kare muhalli ta Majalisar Ɗinkin Duniya, UNEP, ta damu da yawan man fetir da ya malala a Bodo da kuma sauran yankunan Ogoni. A cikin rahoton da ta wallafa a watan Agustan 2011, hukumar ta ba wa gwamnati da kamfanonin mai shawara da su ware dubban miliyoyin dalar Amirka wajen tsabtacen yankin. Sai dai har yanzu gurɓataccen man ne ya mamaye ruwayen yankin.
Hoto: Katrin Gänsler
Ba wanda ya damu da gurɓatar muhalli a Najeriya
Saint Emmah Pii, Basaraken Bodo, ya fusata inda ya ce "Muna mutuwa a nan. Muna shan gurɓataccen ruwa. Muna shaƙan iska mai guba. Laifin man fetir ɗin ne.“ Sai dai in ban da al'ummar Bodo babu wanda ya damu da halin da suke ciki. „Kawo yanzu gwamnati a birnin Abuja da manyan kamfanonin mai ba su damu da matsalolinmu ba“, inji Basaraken ƙauyen.
Hoto: Katrin Gänsler
Ba abin da ke gudana sai da baƙin zinarin
Tun da ta fara haƙo mai a shekarar 1958 Najeriya ta kasance matsayi na shida a jerin ƙasashe mafiya arzikin mai a duniya, inji kamfanin mai na ƙasa a Najeriya wato NNPC. Saboda haka ƙasar ta dogara kacokan a kan baƙin zinarin da ke samar ma ta kashi 90 cikin 100 na kuɗaɗen shiga. Saboda haka ya zama dole a jure wa bututun mai kamar wannan da ke a jihar Rivers.
Hoto: Katrin Gänsler
Rayuwa ƙarƙashin hayaƙin wutar gas
A ko-ina cikin yankin Niger Delta wuta ka iya tashi ba zato ba tsammani musamman ta masu ƙona iskar gas ba tare da la'akari da kusancin wurin da wuraren zaman jama'a ba. Tun a shekarar 1984 a hukumance wata doka ta haramta ƙona gas. Sai dai har yanzu shekaru 28 baya, ba wanda ya kula da ganin an yi aiki da wannan doka.
Hoto: Katrin Gänsler
"Ba wani abin da ya saura mana"
Chukwuma Samuel ya nuna fushinsa game da wutar da ke tashi, wadda a dole da shi da sauran mazauna ƙauyen da ke kusa da garin Egbema ke rayuwa da ita. „Ku dubi mutanen da ke a nan, dukkansu sun yi fushi“, inji shi yana mai nuni da wata ƙaramar kasuwa da yake tsaye gabanta. „Muna jin jiki a nan. Muna ruwa cikin matsatsi. Ba ma ganin ko sisin kwabo daga arzikin man fetir.“
Hoto: Katrin Gänsler
Ya kamata mutane da kansu su yanke hukunci kan abin da suke bukata
Kamfanonin mai ba sa son jin ƙorafin da ake cewa ba sa kula da mutane. Saboda haka kamfanin Shell ke tafiyar da wani shiri wai – Global Memorandum of Understanding, inda yake ba wa ƙauyuka kuɗaɗe tare da ba su damar yanke hukunci kan abin da za su yi da kuɗaɗen. A Fatakwal an sabunta asibitin Obio Cottage Hospital da wannan kuɗi. Majiyata a asibitin sun yaba da wannan aiki matuƙa.
Hoto: Katrin Gänsler
Babu wani tallafi a Bodo
Sai dai a ƙauyen Bodo babu wani taimako da ake samu, inji Kentebe Ebiaridor na ƙungiyar kare 'yancin muhalli ta Environmental Rights Action (ERA). „Mutanen na ganin tamkar an kai su an baro“, inji shi. Babbar shaida a nan ita ce gaɓar kogi da mai ya gurɓata ta.
Hoto: Katrin Gänsler
Tallafin da ake samu shi ne na mai kaɗai
Kasancewa Najeriya na da arzikin mai, 'yan ƙasar na ganin haka ne kawai a tallafin farashin mai da gwamnati ke bayarwa. Ya zuwa ƙarshen shekarar 2011 ana sayar da lita ɗaya na man fetir a kan Naira 65. A farkon shekarar 2012 gwamnati ta soke wani kaso na tallafin. Amma bayan bore da zanga-zanga na tsawon makonni farashin man ya koma Naira 97.
Hoto: Katrin Gänsler
Mafarkin buɗe ƙaramin shago
Franziska Zabbey ba ta ci gajiyar tallafin man fetir ɗin ba. Tana rayuwa ne a kan noma kuma ba safai take barin ƙauyen Bodo ba. Noman ba ya sama mata isasshen kuɗin rayuwa. Franziska ta yi fatan cewa: „Idan kamfanin Shell ya biya mu diyyar muhalinmu da ya lalata, ina iya buɗe wani ƙaraminn shago“. Sauran abubuwa ba su da wata makoma a Bodo.
Hoto: Katrin Gänsler
Sana'arsu a tsawon rayuwa
Duk da cewa da wuya a rayu da sana'ar kamun kafi, amma har yanzu a Bodo ana ci-gaba da kiyaye kwale-kwalen masunya. Sai dai ba a san ranar da za a sake amfani da su ba. Babu wani haske ga hasashen da Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi. Rahoton hukumar UNEP ya nuna cewa za a ɗauki tsawon shekaru 25 zuwa 30 kafin a tsabtace yankin Ogoni daga gurɓataccen mai.
Hoto: Katrin Gänsler
Hotuna 121 | 12
Sama da dalar Amurka miliyan 1000 ne dai kamfanin na Shell ya kai ga batarwa a cikin yankin, amma kuma ba tare da samun tasirin da ake da bukata a cikin aikin yasar dagwalon man fetur din ba. Bayan Ogoni, yankuna da dama a Niger Delta na fuskantar matsalar gurbatar muhallin sakamakon karuwa fasa bututu da kila satar man fetur.
Injiniya Mohammed Lawal tsohon darakta ne a kamfanin man NNPC na kasar, kuma ya ce: "Ko bayan rikicin na Ogoni da akwai sauran tafiya, tsakanin Tarayyar Najeriyar da warware rigingimun da ke tsakanin al'ummar yankin......"
Ya zuwa shekara ta 2018 Najeriyar dai, ta yi asarar da ta kai Naira Triliyan dai-dai har 63 daga tsai da aikin na hakar man na Ogoni. Yankin kuma da ya zuwa shekara ta 1992, ke samar d aganga dubu 28 na man kusan kullum.