1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Ta'addanciAfirka

Halaka tsageru takwas a Najeriya

Suleiman Babayo MAB
September 16, 2025

Sojojin Najeriya sun halaka tsageru masu dauke da makamai takwas yayin fito na fito a yankin arewa maso gabashin kasar mai fama da matsalolin tsaro na tsawon shekaru.

Sojojin Najeriya
Sojojin NajeriyaHoto: Sunday Alamba/AP Photo/picture alliance

Rahotanni daga Najeriya na nuni da cewa dakarun kasar sun halaka sun halaka tsageru masu kaifin kishin addinin Islama takwas ciki har da shugabannin tsagerun na kungiyar ISWAP, lokacin dauki ba dadi a yankin arewa maso gabashin kasar.

Rikici na tsawon lokaci

Mutanen da hare-haren Boko Haram suka shafa

03:59

This browser does not support the video element.

A wannan Talata rundunar sojan ta ce lamarin ya faru a jihar Borno, inda aka dade ana samun kungiyoyin jihadi.

Gwamnatin Najeriya tana fama da kungiyoyin Boko Haram da ISWAP, inda dubban mutane suka halaka kana wasu da dama suka rasa matsugunansu, sakamakon artabu tsakanin dakarun gwamnati da mayakan kungiyoyin tsagerun masu ikirarin jihadi cikin yankin arewa maso gabashin kasar.