1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Kotu ta yi watsi da karar Atiku Abubakar

September 11, 2019

Bayan share awa kusan tara kotun zaben shugaban kasa a Najeriya ta kori karar da dan takarar jam'iyyar PDP na adawa Atiku Abubakar ya shigar na neman kotun ta soke zaben shugaban kasar na 2019.

Nigeria Präsident Buhari
Hoto: Reuters/L. Gnago

Sama da watanni shida bayan zaben gama garin da aka yi a Najeriya kotun da ke sauraron karan zabe ta tabbatar da zabin da aka yi wa Muhammadu Buhari a matsayin shugaban kasa a wa'adi na biyu na mulki a shekara ta 2019. Babban alkalin kotun Muhammed Garba ya yi watsi da karan da jam'iyyar adawa ta Atiku Abubakar ta shigar na cewar a soke zaben saboda zargin da ta yi na magudi. A zaben dai da aka gudanar a watanni shidan da suka wuce Muhammad Buhari shi ya samu nasara da kishi 56% yayin da Atiku Abubakar ya samu kishi 41%.

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani