Najeriya: Kungiyar malamai NUT ta kira yajin aiki
June 1, 2026
Talla
A ranar 15 ga watan Mayu ne dai yan bindiga wadanda sojojin Najeriya suka zarga da cewa mayakan Jihadi ne na Boko Haram suka sace dalibai a makarantu uku a kudu maso yammacin Jihar Oyo.
Sun yi awon gaba da malamai bakwai tare da yara tsakanin 25 zuwa 39 yan shekaru biyu zuwa 16 a cewar Jami'ai. Har yanzu ana ci gaba da neman su.
Kungiyar malaman Firamaren da sakandare ta jihar Oyo ta ce ta dakatar da dukkan ayyuka a makarantu daga wannan Litinin har sai illa ma sha Allahu.