1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Kungiyar Miyetti Allah ta nuna damuwa

Salissou Boukari
January 14, 2018

A yayin da ake cece-kuce kan rikicin Fulani makiyaya da manoma da ya addabi wasu jihohin Najeriya, kungiyar Miyetti Allah ta yi kira game da ganin an hukunta masu laifi.

Nigeria Boko Haram Anschlag Maiduguri
Hoto: Getty Images/AFP

Kungiyar Miyetti Allah ta Fulani Makiya a Najeriya, ta bukaci a hukunta duk wani wanda aka samu da hannu a kashe-kashen da suke faruwa da ake dangata 'ya'yan kungiyar tare da biyan diyya na asarar da ta faru ga mutanen da rikicin ya shafa a jihohin Benue da Taraba.

A taron manema labarai da kungiyar ta kira da marecen wannan Lahadi a birnin Abuja, kungiyar ta nisanta kanta da kokarin da ta ce ana yi na ba ta mata suna a matsayin kungiyar ‘yan tada a Najeriya.