Najeriya: Martani kan kisan Fulani makiyaya
January 26, 2023![](https://static.dw.com/image/49928269_800.webp)
Baya ga Fulani makiyaya akwai Hausawa mahauta da harin ya rutsa da su yayin da wasu da dama suka jikkata. Barrister Bello Danbaba na cikin mutanen da abin ya faru a gaban idanunsu wanda yace akwai kaninsa cikin wadanda aka kashe.
Tun bayan bullo da dokar hana kiwo a fili da gwamnatin jihar Benue ta yi ake fama da rigingimu tsakanin makiyaya da manoma a jihar. Tuni kungiyar Miyetti Allah ta Fulani makiyaya ta mayar da martani inda ta yi Allah wadai da harin tare da neman a yi wa wadanda aka kashe adalci.
Gwamnatin jihar Nasarawa ta nemi da a kwantar da hankali kan cewa za ta dauki matyakin da ya dace domin ana bincike a kan lamarin.
Koda a shekarar 2022 sai da aka samu kai hari ta jirgin sama a kan makiyaya a jihar Nasarawa, abin da ke nuna yanayin rashin tsaron da ake fuskanta. Fulani makiyaya da manoma dai sun dade suna zaman lafiya a tsakaninsu a shekarun da suka gabata, yanayin da ake fatan dawo da shi.