1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya: Matsalar kiwon shanu a Abuja

Uwais Abubakar Idris
September 12, 2025

Gwamnatin Najeriya da hadin guiwar kungiyar Miyetti Allah ta makiyaya sun baiyan sabbin dubarun kawo karshen matsalar kiwon shannu a Abuja da sauran biranen kasar

Yawo da shanu cikingarin Abuja
Yawo da shanu cikingarin AbujaHoto: DW

Shugabanin makiyaya watau ardo ardo a karkashin kungiyar Miyetti Allah da jami'an gwamnatin Najeriya suna kokarin lalaubo mafita daga matsalar baza shannu a kan tituna a Abuja babban birnin tarayyar Najeriya.

Sun yi kokarin jiffar tsuntusu biyu da duste daya domin tsara dabarar ilmantar da yayan makiyaya domin rage yawan yaran da basa zuwa makaranta. 

Karin Bayani:Rikicin Fulani da Makomar kiwo a Najeriya

Yawo da shanu cikin garin AbujaHoto: DW

Mai alfarma sarkin Musulmi Sultan Sa'ad Abubakar na uku wanda ya jagoranci taron da aka yi da wakilan makiyaya a Abuja, ya bayyana muhimmancin matakan da aka dauka domin shawo kan matsalar a matsayin hanyar samun ci gaban kasa..

Karin Bayani:Martanin Fulani ga shawarar gwamnatin Kano

An kafa kwamiti da zai tattara dukkanin korafe-korafe da ardo-ardo suka yi da suka hada da rashin tsaro, cin zarafi daga jami'an tsaro da sauran matsaloli da suke fuskanta. 

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani