Najeriya na shirin kwaso 'yan kasarta daga Afirka ta Kudu
May 4, 2026
Ministar harkokin wajen Najeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu ta sanar shirin duba yiwuwar dawo da 'yan kasar da ke da ra'ayin koma wa gid adaga Afirka ta Kudu sakamakon karuwar hare-hare da ake kai wa baki. Jami'ar diflomasiyyar ta ce tuni aka samu 'yan Najeriya kusan 130 da suka bayyana aniyar komawa gida, kuma ana sa ran adadin zai iya karuwa nan gaba.
Najeriya ta gayyaci jakadan Afirka ta Kudu
Madam Odumegwu-Ojukwu ta kuma jaddada cewa ba za a taba lamunta ba rayuka da dukuyoyin 'yan Najeriya da ke zaune a Afirka ta Kudu su ci gaba da kasancewa cikin hadari.
Bugu da kari ministar ta kara da cewa akalla 'yan Najeriya biyu ne suka mutu sakamakon lamarin na baya-bayan na, inda ta yi zargin cewa wadannan halaye na nuna kiyayya ga baki sun sake tasowa ne gabanin zaben Afirka ta Kudu, inda jam'iyyun adawa masu kyamar baki ke amfani da yanayin domin samun kuru'in jama'a musamman matasa marasa aikin yi.