Najeriya: An gaza cimma matsaya kan kasafin 2016
April 20, 2016An dai share tsawon makonni sama da biyu ana zaman jiran tsamanni ga batun kasafin kudin kasar da ke zaman irinsa na farko ga sabuwar gwamnatin kasar. To sai dai kuma ana shirin kara jira a bangaren talakawa da ke fatan kasafin zai kai ga sauyi na rayuwa da ma rage radadi a bangare na 'yan kasar.
An kammala wani taron majalisar ministoci ta kasar tare da gwamnatin ta Abuja na cewar fa har yanzu da sauran aiki kan kasafin da ke fuskantar kace-nace cikin kasar.
Ministan kasafin kudin kasar Udoma Udo Udoma dai ya fada wa manema labarai cewar har yanzu ana tattaunawa kan kasafin a tsakanin fadar da kuma majalisun da ke kartar kasa ko mutuwa ko yin rai.
"A kan kasafin kudi na shekara ta 2016, har yanzu muna magana. A kan kasafi na shekara ta 2017 dai tunanin shi ne ya kamata a kai shi gaban majalisu a bana domin amincewa kansa ".
Ya zuwa yanzu wata tawaga ta mutane uku da suka hada da shi kansa shugaban kasar Muhammadu Buhari da mataimakinsa da ministan kasafin ne dai ke bin sidira bayan sidira suna nazarin kasafin da ake zargin an lullube shi da cika burin son rai a bangaren 'yan majalisar kasar ta Najeriya.