1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Najeriya za ta bincike zargi take hakkin dan Adam

Englisch-redAugust 5, 2014

Kungiyar kare hakkin bil Adama ta zargi Najeriya da aikata laifukan yaki a yankin arewa maso gabashin kasar

Hoto: REUTERS

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta zargi dakarun Najeriya da ke yaki da 'yan ta'addan Boko Haram a yankin arewa maso gabashin kasar, da aikata laifukan yaki, kamar yadda wasu shaidu da aka tattara na faifan-bidiyo suka nuna.

Tuni mahukuntan Najeriya suka bayyana kaddamar da bincike, kan lamarin. Kungiyar Boko Haram mai kaifin kishin Islama ta yi kaurin suna wajen aiwatar da ayyukan rashin imani kan mutane musamman a yankin arewa maso gabashin kasar ta Najeriya.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Usman Shehu Usman