Nasarar kafa gwamnatin hadakar Jamus
March 8, 2018Talla
Ana ci gaba da samun martani mabanbanta game da matakin samun matsaya na kafa gwamnatin hadaka, watanni bayan zaben kasa baki daya da ya gudana. Jam'iyyun siyasa na kasar ta Jamus wadanda ke cikin majalisar dokoki na sahun gaba wajen mayar da martani kan kafa gwamnati hadakar da mambobin jam'iyyar SPD suka kada kuri'ar amincewa domin shiga gwamnatin tare da CDU/CSU da Shugabar gwamnati Angela Merkel ke jagoranci.