1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Kungiyar tsaro ta Nato zata gudanar da taro a Brussels

Zulaiha Abubakar
December 4, 2018

Rahotanni daga Brussels sun baiyana cewar ministocin harkokin kasashen wajen kungiyar tsaro ta NATO zasu gudanar da wani taro game da zargin da ake yiwa Rasha na karya yarjejeniyar makamai masu linzami .

Brüssel Jens Stoltenberg, NATO-Generalsekretär
Hoto: picture-alliance/Anadolu Agency/D. Aydemir

A watan Maris din wannan shekara ne Rasha ta kaddamar da wani sabon makami mai linzami mai lakabin Novator al'amarin da Amirka ta baiyana da karya ka'ida tare da yin barazanar ficewa daga kungiyar tsaron, kodayake har ya zuwa wannan lokaci Rasha na kare kanta daga zargin karya ka'idodin makamai da kungiyar tsaron tayi tanadi tun a shekara ta 1987.

Yayin taron dai ana sa rai ministocin harkokin wajen kungiyar da yawansu yakai 29 zasu tabo batun rikicin daya kunno kai tsakanin Rasha da Ukraine bayan da Rasha ta kame jiragen ruwan kasar ta Ukraine bisa zargin su da wuce iyaka.