NATO: Cigaba da yaki da ta'addanci
September 11, 2021![NATO Secretary General Jens Stoltenberg](https://static.dw.com/image/58936598_800.webp)
Talla
Jens Stoltenberg ya sha wannan alwashin ne yayin nuna ban girma ga wadanda harin ta'addancin ranar 11 ga watan Satumbar shekarar 2001 ya rutsa da su a cibiyar kasuwancin ta duniya da ke Amirka.
Yayin bikin tunawa da ranar a Hedikwatar kungiyar da ke birnin Brussels fadar gwamnatin kasar Beljium, Stoltenberg ya ce kungiyar zata cigaba da taka rawar da ta ke yi a yaki da ta'addanci.
A yayin bikin an yi kasa-kasa da tutocin kawance 30 don karrama kimanin mutum dubu uku da suka mutu a harin da Al-Qaeda ta kai, hari mafi muni a tarihin Amirka. Amirka da kawancen NATO dai sun mamaye Afganistan bayan harin a wancan lokacin, tare da kwace ikon kasar a hannun kungiyar Taliban da ke da tsattsaurar ra'ayin addinin Islama.