Netanyahu ya goyi bayan 'yan kasar Iran da ke zanga-zanga
January 5, 2026
Talla
Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana goyon bayansa ga al'ummar Iran, yana mai cewa duniya na iya ganin manyan sauye-sauye a kasar.
Ya yi wannan jawabi ne a farkon taron majalisar ministoci a birnin Kudus, inda ya ce Isra'ila na tare da burin ‘yan Iran na samun ‘yanci da adalci da ma dimukuradiyya.
Kalaman nasa na zuwa ne a yayin da ake ci gaba da zanga-zangar adawa da matsin tattalin arziki a Iran din.
Firaminista Benjamin Netanyahu ya kuma ce akwai yiyuwar ‘yan Iran su dauki makomarsu a hannunsu.
A shekarar da ta gabata, Isra'lar ta yi arangama da Iran na tsawon kwanaki 12, tare da kai hare-hare kan wasu muhimman wuraren nukiliya, tana zargin Tehran da shirin kera makaman nukiliya.