Sojoji sun harbe mahara da dama a Nijar
January 10, 2020Talla
Wani babban jami'in a ma'aikatar tsaro a jamhuriyar Nijar Sulaimane Gazobi ya shaiadwa manema labarai yadda martanin da sojoji suka mayar tare da tallafin jiragen kasar da na abokan hulda ya taimaka wajen korar ‘yan ta'addan tare da nasarar harbe 63 daga cikinsu. Wannan dai shi ne hari na farko da ‘yan ta'addan suka kai a cikin wannan sabuwar shekara ta 2020.