1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar: Malaman kwantaragi sun koka kan albashi

Mahaman Kanta
January 14, 2022

A jamhuriyar Nijar malaman makaranta sun ja zare da hukumomi kan rashin samun albashi a kan kari kamar sauran ma'aikata.

Wasu yara yan makarantar firamare a cikin aji
Hoto: Luc Gnago/REUTERS

Wannan matsala ta malamai 'yan kwantiragi dai, ta jima ta na janyo cece-kuce a Jamhuriyar ta Nijar. Matsalolin dai suan hadar da biyansu albashin da bai taka kara ya karya ba, kana kuma akan biya su albashin a makare ba tare da sauran abokan aikinsu na din-din-din ba duk da cewa sune ke da kaso sama da 70 cikin dari na adadin malaman makarantun firamare da na gaba da firamare a Jamhuriyar ta Nijar.

Koda yake a yayin rantsar da shi, Shugaba Mohamed Bazoum da shi ma ya kasance tsohon malamin makaranta a Jamhuriyar ta Nijar, ya sha alawashin shawo kan matsalolin da ilimi ke fuskanta a kasar ciki kuwa har da alkawarin da ya dauka na mayar da malaman kwantiragin zuwa na din-din-din.

Sai dai har kawo yanzu ba a kai ga cika musu wannan buri nasu ba, koda yake mahukuntan sun nunar da cewa suna sane kuma suna daukar matakan da ya dace domin shawo kan matsalar.
 

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani