1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
Salon rayuwaNijar

Kalubalen matasan Nijar a Mali

Salissou Boukari LMJ
November 5, 2025

Daruruwan matasa da ke zuwa Mali neman zinare daga Jamhuriyar Nijar, na komawa cikin mawuyacin hali sakamakon matsalar tsro.

Nijar | Matasa | hakar Zinare | Mali
Matasa masu hakar zinari a Mali na komawa gida Nijar saboda matsalar tsaroHoto: Maxwell Suuk/DW

'Yan ta'addan na kwacewa matasan kudin da suke samu, abin da suka ce yana tilasta wasu da dama daga cikinsu da ba su da kudin komawa gida makalewa cikin halin ha'ula'i. Ana iya cewa sannu a hankali zuwa ci-rani wajen ko buda da matasa da dama 'yan Nijar ke yi zuwa kasar Mali na zama wani babban kalubale, sakamakon tarin matsalolin da suke fuskanta.

A birnin Yamai dai a tashshin mota da masu zuwa yanki Gao na kasar Mali, mafi yawan matasan da suka koma gidan na cikin mawuyacin hali. Daga Nijar dai daruruwan matasa daga jihohin Damagaram da Maradi da Tahoua da Tillabery, sune suka fi yawa daga cikin masu zuwa neman zinare a Mali. Salissou wani matashi da shi ma ya koma gida daga kasar ta Mali ya ce, idan ka yi dace zaka samu alkhairi sosa a iakin hakar zinaren. Sai dai ya ce da suna da abin yi a gida Nijar, ba za su rinka tafiya ci-ranin ba, sabota tarin kalubalen da ke cikin aikin.

Tsallake zuwa bangare na gaba Bincika karin bayani