1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Nijar ta ce a fitar da jakadan Faransa daga kasar

August 31, 2023

Majalisar mulkin sojin Nijar ta bayar da umurni ga 'yan sandan kasar da su fitar da jakadan Faransa daga kasar tare da janye dukannin wata kariya da yake samu ta diflomasiyya.

Hoto: Mahamadou Hamidou/REUTERS

Sanarwar ta birnin Yamai ta ce an soke dukkanin takardun diflomasiyyar da kuma Visarsa da na iyalansa. A baya dai, gwamnatin sojin kasar da ta hambarar da Mohamed Bazoum daga mulki ta bai wa Sylvain Itte sa'o'i 48 da ya fice daga kasar a makon da ya gabata. Sai dai Faransa ba ta yi wa jakadan nata kiranye ba bayan da wa'adin ya cika a ranar 28 ga watan Agusta.

Karin bayani: Sojojin Nijar sun kori karin wasu jakadu daga kasar

Cikin wata sabuwar sanarwa da Faransa ta bayar a wannan Alhamis, ta jadadda cewar har yanzu tana kan bakarta na cewar jakadanta zai ci gaba da aiki a Yamai saboda ba ta amince da sojojin a matsayin jagoroin Nijar na halak da malak ba. Dangantaka dai na kara yin tsami tsakanin Jamhuriyar Nijar din da kuma uwargijiyarta Faransa.

Karin bayani: Sabuwar baraka tsakanin Nijar da Faransa