Nijar: 'Yan kwadago na so a yi yajin aiki
April 28, 2016Talla
Shugabannin kungiyoyin fararen hula na da 'yan kwadago a Nijar sun nemi masu sana'a da su kauracewa wuraren sana'o'insu don nuna rashin jin dadinsu game da rashin aiwatar da dimokadiyya kamar yadda ya dace a kasar wanda gwamnatin Shugaba Issoufou Mouhammadou ke yi.
Wakilinmu na Yamai Mahamman Kanta ya ce kungiyoyin sun ambata hakan ne dazu a wani taron manema labarai da suka kira. To sai dai duk da wannan kira da 'yan kwadagon suka yi, 'yan kasuwa a babbar kasuwar da ke birnin Yamai na cigaba da kasuwancinsu.