Nuri Al Maliki ya ziyarci Turquia
August 7, 2007Irak da Turkiyya sun rattaba hannu a kan wata yarjeniya, ta haɗa ƙarfi domin yaƙar yan tawayen Ƙurdawa na PKK.
An cimma wannan yarjejeniya a sakamakon ziyara aikin da Praminista Nuri Al Maliki ya kai a birnin Ankara yau talata.
Ƙasashen 2 na zargin yan tawayen Ƙudawa na PKK, ta tada masu hargitsi, a game da haka ya zama wajibi inji sanarwar, su gama ƙarfi da ƙarfe, domin maido kwanciyar hankali a arewancin ƙasar Irak, yankin da yan tawayen ke anfani da shi, domin kai hare-haren.
Nur Al Maliki ya gudanar da wannan ziyara, a daidai lokacin da rikicin siyasa ke ƙara tsamari a birnin Bagadaza, inda wasu ƙarin ministoci 4 su ka yi murabus daga gwamnati.
Dag jimilar ministoci 40 da wannan gwamnati ta ƙunsa, a halin yanzu 17 su ka yi murabus daga muƙamin su.
A wani labarin kuma, ƙasar Danmark ta yanke shawara janye dakarun ta daga Irak.