1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Odinga ya kira zanga-zanga a ranar zabe

Ramatu Garba Baba
October 18, 2017

Madugun adawa a Kenya Raila Odinga ya yi kira na gudanar da zanga-zanga a ranar da hukumar zaben kasar ta tsayar don sake zaben shugaban kasar da aka soke a baya bisa zargin cewa an tafka magudi.

Kenia nach der Annulierung der Präsidentenwahl | Raila Odinga
Hoto: picture alliance/AP Photo/B. Curtis

Raila Odinga a yayin jawabinsa ya ce gangamin na ranar 26 ga wannan watan na Oktoba zai kasance wanda ba a taba gani ba a kasar, a makon da ya gabata dan takarar kujerar shugaban kasar ya sanar da janye takararsa a zaben da aka bukaci maimaitawa bisa wasu manyan kura-kurai, sakamakon zaben na farko ya bai wa shugaba mai ci Uhuru Kenyatta nasara.

A daya bangaren kuwa, hukumar zabe a wannan Laraba ta gargadi 'yan takara da ma sauran shugabani na jam'iyyun siyasa da su guji tsoma baki cikin lamurran hukumar a yayin da ta ke kokarin ganin ta gudanar da sahihiyar zabe, shugaban hukumar Wafula Chebukati ya yi gargadin ne a yayin ganawa da manema labarai gabanin zaben na mako mai zuwa inda ya nuna yatsa ga jagororin jam'iyyun siyasa a kenya da ya ce sun kasance babban barazana ga demokradiyar kasar.

 

Tsallake zuwa bangare na gaba Babban labarin DW

Babban labarin DW

Tsallake zuwa bangare na gaba Karin labarai daga DW