1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Pakistan: Cinkoso jama'a ya janyo asarar rayuka

Abdourahamane Hassane
March 31, 2023

Akalla mutane tara ne suka mutu a wani turmutsitsin da ya barke a birnin Karachi da ke kudancin Pakistan,yayin da jama'a suka garzaya zuwa wata masana'anta da aka shirya rabon sadaka na azumin Ramadan.

Pakistan Krankenhaus in Karatschi bei einer Massenpanik während einer Ramadan-Almosenverteilung
Hoto: ASIF HASSAN/AFP

Turmutsitsin ya faru ne a lokacin da mata mabukata da ‘ya'yansu suka cincirindo a masanantar.inda cinkosso jama'a ya yi yawa.Yanhzu haka an kai gawarwakin mata shida da yara uku zuwa asibiti in ji kakakin 'yan sanda birnin na karashi Muhammad Farukh.