SiyasaAfirka
Pekka Haavisto ya yi kira da a tsagaita bude wuta
April 15, 2026
Talla
Fiye da fararen hula 50,000 sun mutu a fadin kasar Sudan sakamakon yakin. Sama da 'yan kasar miliyan 14 sun yi hijira; lamarin da ya haifar da daya daga cikin matsalolin jin kai da gudun hijira mafi girma a duniya.
Yanzu haka dai masu bayar da agaji na taro a birnin Berlin fadar gwamnatin Jamus. Berlin din ta yi alkawarin dala miliyan 24 a bana, bayan Yuro miliyan 155 da ta bayar a bara.
Ana kuma tattauna yadda za a ci gaba da samar da tallafin gaggawa tare da bullo da sabbin dabarun sake zaman sulhu tare da tallafin Masar da Saudiyya da Hadaddiyar Daular Larabawa.