Rahoton shekara shekara na ƙungiyar kare haƙƙoƙin yan jarida ta dunia IPI
March 30, 2006A sahiyar yau ne a birnin Vienna,ƙungiyar kare haƙƙoƙin yan jarida da dunia, wato IPI, ta bayyana rahoton ta na shekara da ta gabata.
Rahotion yace, a shekara ta 2005, baki ɗaya yan jarida 65 su ka rasa rayuka, a bakin aiki, a ƙasashe daban daban na dunia.
Ƙasar Irak ke sahun gaba, daga jerin ƙasashe 175 da ƙungiyar ta gudanar da bincike.
A wannan ƙasa, yan neman rahoto 23 su ka riga mu gidan gaskiya, a shekara ta 2005.
Sannan 9 a ƙasar Phillipines, 3 a Bangladesh, da Haiti sai kuma, yan jarida 27, a cikin sauran wasu ƙasashe 18.
Bayan mace-mace, da ake samu a cikin wannan aiki, rahoton ya bayana ƙaruwar barazana, da tauye haƙƙoƙi da yan jaridar ke fuskanta, daga gwamnatoci, da ma wasu jama´a.
Mussamman ƙungiyar IPI, ta yi suka da kakkausar harshe ga ƙasar China, wadda ta yi ƙaurin suna ta wannan fanni.
An girka IPI, tun shekara ta 1950 a ƙasar Amurika, kuma a halin da a ke ciki, ta na da rassa, a ƙasashe 120 na dunia.