1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rarrabuwar kawunan kasashen Musulmai kan Siriya

August 14, 2012

Shugabannin musulmai dake taro a Makka don tattauna al'amuaran kungiyar su ta OIC, sun fiskanci tada jijiyar wuya bisa rikicin kasar Siriya

Egyptian Foreign Minister Mohammed Kamel Amr (C) talks on his phone upon his arrival to attend a preparation meeting of foreign ministers of the Organisation of Islamic Cooperation (OIC) in the Saudi coastal city of Jeddah on August 13, 2012. Leaders of Muslim countries, including Iran's pro-Syrian President Mahmoud Ahmadinejad, are due to gather for an extraordinary summit called by Saudi King Abdullah who is pushing to mobilise support for the Syrian rebellion. AFP PHOTO/FAYEZ NURELDINE (Photo credit should read FAYEZ NURELDINE/AFP/GettyImages)
OIC Treffen Außenminister Ägypten Mohammed Kamel AmrHoto: Getty Images/AFP

Shugabannin kungiyar kasashen Musulmi ta duniya OIC na gudanar da wani taro yanzu haka a birnin Makkah na kasar Saudi Arabiya inda su ke tattaunawa game da makomar Siriya a cikin kungiyar.

Gabanin taron dai, ministotocin harkokin wajen kungiyar da ke da mambobi 50 da bakwai sun bada shawarar korar Siriya daga kungiyar.

Shugaban kasar Siriya Baschar al-Assad da sarkin Abdullah ibn Abd al-Aziz na Saudizza lokacin da suke dasawaHoto: AP

Sarki Abdallah Bin Saud na kasar ta Saudiyya ne dai ya bada shawarar kiran taron a wani yunkuri da ake ganin na karfafa gwiwar 'yan tawayen Siriya ne, a yunkurin da su ke yi na ganin shugaba Bashar al-Assad ya yi adabo da karagar mulki.

To sai dai duk da kasarin mabobin kungiyar na goyon bayan wannan matsayin da Sarki Abdallah ya dauka, a bangare guda Iran wadda shugabanta Mahmud Ahmedinijad ke hallartar taron ba ta goyon bayan batun korar Siriyan daga kungiyar. Wannan ya nuna irin rarrabuwar kawuna tsakanin ma biya darikar Sunni da wadanda ke bin darikar Shi'a.

Kazalika Iran din ta nuna rashin amicewar da abin da ta kira kokarin mahukuntan Saudiyyan da na Qatar da kuma Turkiyya na rura wutar rikicin Siriya wanda ke cigaba da janyo asarar rayuka.

Mawallafi: Mahmud Yaya Azare

Edita: Usman Shehu Usman