Rasha ta karfafa kawance da Afirka
February 9, 2023![Sudan Besuch Außenminister Russland Lawrow](https://static.dw.com/image/64659570_800.webp)
Ministan ya ce, kasar Rasha za ta iya karfinta don ganin MDD ta cire takunkumin da aka aza wa kasar Sudan. Sergei Lavrov ya bayyana haka a Khartoum babban birnin kasar Sudan, yayin ziyarar aiki ta kwanaki biyu da ya kai a Sudan. Ministan harkokin wajen Rasha a ziyarar tasa, ya kuma gana da shugaban kasar Sudan Abdel Fattah al-Burhan, inda suka tattauna kan mahimman batutuwa na kara karfafa hulda tsakanin kasashen biyu. Ziyarar kasar Sudan, ita ce kasa ta uku da Lavrov ya ziyarta a Afirka, bayan kasashen Mali da Murtaniya. Kasar Rasha dai na kara karfafa kusancinta da kasashen Afirka, yayin da kasashen Yamma ke gograrin maida ita saniyar ware, ko da a watan jiya ministan harkokin wajen na Rasha Sargei Lavrov ya ziyarce kasashen Eritrea, Angola, Eswatini Afirka ta Kudu. A Watan Juli kuwa za a yi taron hadakar Rasha da kasashen Nahiyar Afirka.