1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rasha za ta shugabanci kwamittin sulhu na MDD

April 1, 2023

Rasha ta karbi shugabancin karba-karba na kwamittin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya. Fadar Kremlin ta ce ta shirya sauke nauyin da ya rataya a wuyanta na shugabancin.

USA New York | UN-Sicherheitsrat
Hoto: Ed Jones/AFP/Getty Images

Kasar Amirka ta bukaci Rashar ta gudanar da shugabancin bisa kwarewa yayin da ta yi ikrarin cewa babu wata hanya da za a iya bi wajen hana Rasha jan ragamar kwamittin, duk da kokarin da Ukraine ta yi na ganin hakan bai yiwu ba. Ministan harkokin wajen Ukraine, Dmytro Kuleba ya bayyana shugabancin Rasha a kwamittin a matsayin babban abun kunya ga duniya kana ya bukaci kasashen mambobin kwamittin da su takawa Rashar birki idan ta yi yunkurin wuce gona da iri. Rasha dai za ta ja ragamar kwamittin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya a watan Aprilun nan da muke ciki kafin ta mika shugabancin ga kasar Switzerland.