SiyasaAfirka
Iran ta kai hari kan Kurdawa
September 29, 2022![](https://static.dw.com/image/63275974_800.webp)
Talla
A wata sanar da Ma'aikatar harkokin wajen Amirka ta fitar, ta ce, wani dan kasar na daga cikin wadanda suka mutu a sakamakon wasu jerin hare-hare da rokoki da rundunar sojin Iran ta kai a yankin Kurdistan na kasar Iraki. Sanarwar ta ce, ba za ta yi karin bayani kan harin a yanzu ba, saboda dalilai na tsaro.
Akalla mutane goma sha uku aka tabbatar sun salwanta a hare-haren da Iran ta kaddamar a yankunan da ta kira da sansanonin kungiyoyin abokan hamayyarta watau Kurdawa da ta zarga da hannu a goyon bayan zanga-zangar da ke gudana a yanzu haka a Tehran da sauran sassan kasar kan kisan matashiya Mahsa Amini.