1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikici tsakanin Fatah da Hamas na barazanar zama wani yakin basasa

June 12, 2007

Fada ya kazanta tsakanin kungiyoyin Falasdinawa da ba sa ga maciji da juna wato Fatah da Hamas a Zirin Gaza. Rahotanni sun ce an halaka mutane 20 a sabon fadan da ya barke da sanyin safiyar yau talata. An lalata gidan FM Falasdinawa Isma´il Haniya a wani hari da aka kai kan gidan a yau. Jim kadan bayan haka wasu ´yan bindigan kungiyar Hamas sun farma hedkwatar jami´an tsaron kungiyar Fatah a birnin Gaza, bayan wani gurnati da aka harba a kusa da ofishin shugaban Falasdinawa Mahumd Abbas. Shugaban na Falasdinawa yayi kira da a kwantar da hankula. Sannan a lokaci daya ya zargi Hamas da kokarin kwace mulki da karfin tuwo a Zirin Gaza. A kuma halin da ake ciki kakakin kungiyar Fatah ya ce a wani lokaci a yau kwamitin tsakiya na kungiyar zai yi wani taro don tataunawa ko zasu saura cikin gwamnatin hadin guiwa da suka kafa da Hamas a cikin watan maris a wani mataki na kawo karshen tashe tashen hankula na cikin gida.