1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin addini a Masar

January 3, 2011

'Yan siyasa da Kiristoci 'yan ɗarikar Coptic a Jamus sun yi kira da bawa Kiristoci kariya a Masar

Zanga-zangar yin tir da harin da aka kai kan Kiristoci 'yan Coptic a MasarHoto: picture alliance/dpa

Shugabannin siyasa da na addini a nan Jamus sun yi kira ga gwamnatin Masar da ta ƙara ɗaukar matakan ba da kariya ga Kiristoci tsiraru a ƙasar. A jiya daddare an sake yin arangama tsakanin 'yan sanda da ɗaruruwan Kiristoci mabiya ɗarikar Coptic a Masar dake zanga-zangar yin tir da harin ƙunar baƙin wake da aka kai kan wani coci dake a birnin Alexandria a jajebaren ranar sabuwar shekara. Volker Kauder shugaban ɓangaren jam'iyar CDU a majalisar dokokin Jamus ta Bundestag ya ce ya kamata Jamus ta ƙara matsawa Masar lamba domin ta yaƙi masu tsattsauran ra'ayin addini. A kuma halin da ake ciki shugaban cocin Coptic a Jamus, Anba Damian ya ce 'yan sandan tarayya sun gargaɗe shi game da barazanar kai hare hare kan 'yan Coptic a Jamus a wannan wata.

"'Yan sandan tarayya sun yi gargaɗin cewa a intanet ana yaɗa wata maƙarƙashiya ta kaiwa majami'un Coptic a ƙasar harin ta'addanci daga ranar 6 zuwa 7 ga watan Janeru wato ranar bikin Kirsmettin mu."

Cocin na Coptic ya bayyana wannan harin a Alexandria da cewa sakamakon ƙyamar da ake nuna musu da ya yawaita a watannin baya-bayan nan.

Mawallafi: Mohammad Nasiru Awal

Edita: Yahouza Sadissou Madobi