1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin Darfur na ƙasar Sudan

May 19, 2007

Tawagar haɗin gwiwa, da ta ƙunshi wakilan majalisar Ɗinkin Dunia, da na ƙungiyar taraya Afrika, na ci gaba da tantanawa da ɓangarori daban-daban masu yaƙar juna, a ƙasar Sudan ,da zumar samar da kwanciyar hankali mai ɗorerwa.

Jan Eliyasson, da Salim Ahmed Salim, da ke jagorantar wannan tawaga, sun yi taron manema labarai a birnin Khartum, inda su ka bayyana takaici, a game da hauhawar yaƙe-yaƙen ƙabilanci a yankin Darfur.

A ganawar da su ka yi da hukumomin Khartum, jami´an 2, sun, buƙaci dakarun gwamnati su daina kai hare-hare ga garuruwan Darfur.

A ɗaya hannun, sun yi kira ga yan tawayen yanki, su tsagaita wuta.

A mako mai zuwa, Majalisar Ɗinkin Dunia,ta ambata aika wata tawaga ta mussamman, a ƙasar Tchad, domin ganawa da hukumomin N`Dajmena, a kan rundunar haɗin gwiwa, da Majalisar zata tura, domin shiga tsakanin a wannan yanki mai fama da rigingimu.