Rikicin Irak
November 15, 2006Pramninistan ƙasar Irak, Nuri Al Maliki ,ya umurci jami´an tsaro, su shiga farautar yan ƙunar baƙin waken da su ka sace wasu mutane, jiya, a birnin Bagadaza da rana gatse-gatse.
Wannan al´amari, mai ban mamaki, ya nunar da cewa, ko shakka babu, akwai hannun jami´an tsaron Irak, a hare haren da ake kaiwa wannan ƙasa.
Binciken da wasu daga cikin su ke gudanarwa, tamkar a yi sata da su ne, a kuma koma bin sau tare da su inji Nuri Al-Maliki.
A ranar yau laraba, yan takifen, su sako mutane fiye da 20, amma har yanzu, akwai sauran wasu cikin hanun su.
A yayin daya ke bayani da yan jarida, Praministan Irak, ya nuna matuƙar damuwa ga halin da ƙasar Irak ta tsinci kanta a halin yanzu.
A dangane da wannan rikici da ke ɗaiɗaita Irak, Majalisar Dokin ƙasar Russia, ta hiddo wata sanarwa a yau laraba , inda ta ce hukunci kissan da a ka yankewa tsofan shugaban ƙasa Saddam Hussain, zai zama wata sabuwar kafa ta ƙara durmuya Irak, cikin halin ni yasu, a game da haka, Majalisar Duma, ta yi kira ga kotuna da magabatan Irak, su ɗauki matakin hana zartar da wannan hukunci.