1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin makashi tsakanin Isra'ila da Masar

April 23, 2012

Priyiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bayyana cewar taƙaddamar da ta kunno kai tsakanin ƙasar ta Isra'ila da Masar dangane da sayar da isakar gas ba ta da nasaba da siyasa.

epa02564963 A view showing huge flames erupting from a blast at Egyptian gas pipeline supplying Israel and Jordan in Al-Arish, Egypt, 05 February 2011. An explosion occurred Saturday at an Egyptian pumping station in the Sinai Peninsula supplying natural gas to Israel and Jordan. Egyptian state television said the explosion was a 'terrorist operation' and blamed 'saboteurs' for the incident, saying they had taken advantage of the country's ongoing political unrest. EPA/STR
Hoto: picture-alliance/dpa

Mr. Netanyahun ya bayyana hakan ne bayan da aka fara hasashen cewar dangantaka tsakanin ƙasashen biyu ta fara tsami, inda ya ce lamarin ya auku ne sakamakon wani saɓani na kasuwanci tsakanin ɓangarorin biyu.

A nata ɓangare, ƙasar ta Masar wadda ita ce ke samawa Isra'ilan kashi arba'in cikin ɗari na iskar gas ɗin da ta ke amfani da shi, ta ce lamarin ba haka ya ke ba, inda ta ƙara da cewar ta yi hakan ne saboda Isra'ila ta yi karen tsaye ga yarjejeniyar da su ka ƙulla game da cinikin isar Gas ɗin da ma dai tura shi ƙasar ta Isra'ila.

Mawallafi : Ahmed Salisu
Edita : Abdullahi Tanko Bala