SiyasaAfirka
Rikicin Sudan ya kazance
October 27, 2025
Talla
Hukumar kare hakkin dan Adam ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadi a wannan Litinin kan hali da ake ciki a garin El-Fasher da mayakan RSF da ke fafatawa da dakarun gwamnati suka bayyana kwacewa. Tun watan Mayu na shekarar da ta gabata ta 2024 ake kai ruwa rana tsakanin bangarorin domin kwace iko da garin na El-Fasher wanda ke zama gari mai tasiri a yammacin Darfur.
Yuwuwar aika ta'asa
Shugabar hukumar kare hakkin dan Adam na majalisar Volker Turk ya fitar da wata sanarwar da ke nuni da yuwuwar samun aikata ta'asa daga bangaren mayakan da suka kwace iko da garin na El-Fasher.
Tun watan Afrilun shekara ta 2023 fada ya barke tsakanin sojojin gwamnatin Sudan da mayakan rundunar RSF.