Rikicin yankin Darfur
December 13, 2005Shugaban hukumar kulla da yan gudu hijira, ta Majalisar Dinkin Dunia, Antonio Guteres, ya bayyana kara gurbacewar zaman lahia a yankin Darfur na kasar Sudan.
A cikin wannan yanayi, ma´aikatan bada agaji na Majalisar Dinkin dunia ,da na kungiyoyi masu zaman kansu, na aiki jinni kan aikafa, ta la´akari da barazanar kissa, da su ke fuskanta a ko wane lokaci.
Hanya daya da ta cencenta a halinyanzu itace ta anfani da jiragen sama masu durra angulu domin kai agaji a wassu yankuna.
Antonio Guteres ya kira, ga komiti Sulhu na Majalisar Dinkin Dunia, da ya kara basira ta fannin warware wannan rikici.
A wani rahoto ta ta fido jiya kungiyar kare hakokin bani Adama ta Human Rights Watch, ta zargi gwamnatin Soudan da babban lefi a cuikin ta´assar da ke wakana a yanki Darfur.