1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Rikicin yankingabas ta tsakiya

November 13, 2006

Ministocin harkokin wajen kasashen Larabawa da suka hadar dana yankin Palasdinawa ,sunyi kira da a kaddamar da wani taro na musamman adangane da sabon tsari na wanzar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya,wanda zai samu halartabn manyan kasashe masu fada aji na mdd da wakilan larabawa da Izraela.Bugu da kari ´ministocin a wani taron gaggawa da suka gudanar a birnin Alkhahira,sun yi alkawarin kawo karshebn takunkumin tallafin kudade da aka dorawa yankin palasdinawa ,sakamakon nasaran da yan hamas suka samu a zaben watan janairu.Ministocin larabawan sun bayyana muradinsu na bawa hukumar palasdinu tallafi ,ba tare da laakari da manufofin Amurka dana sauran kasashen turai ba,inji babban sakataren kungiyar kasashen Amr Moussa.