1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Ruwanda na shirin karbar wadanda Amurka za ta sallama

May 5, 2025

Kasar Ruwanda na shirye-shiryen game da karbar wadanda AMurka ta shirya sallama daga kasar, bayan tsare-tsaren da suka zo jim kadan da kafuwar gwamnatin Shugaba Donald Trump.

Shugaba Paul Kagame na kasar Ruwanda
Shugaba Paul Kagame na kasar RuwandaHoto: Lim Yaohui/Newscom/Singapore Press Holdings/IMAGO

Ruwanda na cikin matakin farko na tattaunawa kan yadda za ta karbi baki 'yan Afirka da Amurka za ta tasa keyarsu zuwa gida.

Cikin 'yan shekarun nan dai, kasar ta Ruwanda ta kasance wani sansani da kasashen yammacin duniya ke amfani da ita wajen sauke mutanen da suka ji ba su bukatar zamansu a kasashen.

Kasar dai na yin hakan ne kuwa, duk da damuwar da take nunawa a gefe guda kan yadda hakan ke cin karo da dokoki na 'yancin bani Adama.

A shekara ta 2022 ma dai Ruwandar ta sanya hannu kan yarjejeniya da Burtaniya, inda ta karbi wasu dubban masu neman mafaka, kafin daga bisani kasar ta Burtaniya ta janye batun jim kadan bayan rantsar da Firaminista Keir Starmer.

Jim kadan bayan kama madafun iko cikin watan Janairu ne dai, Shugaba Donald Trump na Amurka ya kaddamar da aniyar share baki 'yan kasashen waje tare da kawo tsarin inda za a sake tsugunar da su.