1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Sabani kan taron magance rikicin Siriya

January 20, 2014

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya ya gayyaci Iran taron magance rikicin Siriya.

Hoto: UN Women Gallery

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Ban Ki-moon ya gayyaci kasar Iran zuwa taron neman magance rikicin kasar Siriya, da zai gudana a wannan mako a kasar Switzerland. Ban, ya nunar da cewa akwai rawar da Iran za ta iya takawa wajen warware matsalar.

A cikin martanin da ta mayar, babbar kungiyar 'yan tawayen Siriya, ta yi barazanar janyewa daga zuwa taron idan ba a janye wannan gayyata ba. Kasar ta Iran ta kasance babbar mai dasawa da gwamnatin Siriya ta Bashar al-Assad. Kasar Amirka tana cikin masu adawa da zuwan Iran zauren taron.

Mawallafi: Suleiman Babayo
Edita: Saleh Umar Saleh