Shugaban gwamnatin Jamus da za a samar a zaben tarayya na 2025 zai yi wani sabon tsari a kan manufofinsa na ketare, inda zai nisanta kansa daga Amurka tare da rungumar tsarin samar wa kasa tsaro.
Olaf Scholz na jam'iyyar SPD da Friedrich Merz na jam'iyyar CDU na daga cikin manyan 'yan takara a zaben Jamus na 2025Hoto: Michael Kappeler/dpa-Pool/dpa/picture alliance
Talla
Sabuwar gwamnatin Jamus za ta fuskanci kalubale masu tarin yawa a kan manufofinta na ketare bayan sabon zaben 2025. Akwai batu na sauyin alkibla, wadanda akasarinsu za su kasance sabbi a fannoni daban-daban, inda Jamus za ta yi ban kwana da rawar da take takawa na matsayin kasa mai fada a ji kuma mafi karfin tattalin arziki a tnahiyar Turai.
Shekaru da dama bayan yakin duniya na biyu, ministocin harkokin wajen Jamus sun yi tsammanin za su kasance a kan matsayinsu mai martaba, na jan akalar lamuran da suka danganci Turai. Duba da dangantakarta da kasashen yammacin duniya, Jamus ta ci gaba da zama mai ra'ayin bangarori daban-daban, kana mai fafutukar tabbatar da dimukuradiyya da bin doka da oda, inda ake zartar da shawarar manufofin harkokin waje tare da hadin gwiwar abokanta na Yamma, yayin da Amurka ke da alhakin tsaron kasar.
Amma ya ya labarin yake a yanzu?
A taro kan tsaro na birnin Munich, sabon mataimakin shugaban Amurka J.D. Vance ya sanar da cewa dole ne Turai ta dauki nauyin tsaron kanta. Wannan magana ce da ta bata ran shugaban jam'iyyar CDU kuma wanda ake ganin zai iya zama sabon shugaban gwamnati Friedrich Merz.
Friedrich Merz ya yi Allah wadarai da shisshigin Amurka a zaben JamusHoto: Kay Nietfeld/dpa/picture alliance
A wata hira da tashar DW, Merz ya ce: "Eh, lallai yau ranar tarihi ne a gare mu. Ana dasa ayar tambaya game da tsayawar Amurka kuma Amurkawa na saka shakku game da nuna dimukuradiyya. A bayyana yake, ana mana katsalandan a cikin zaben, ciki har da yadda ake tafiyar da jam'iyyun dimukuradiyya da sauran su. Kuma dole in ce, abun damuwa ne. Ban yi mamaki wannan sanarwar ba."
Duk wannan yana faruwa ne a cikin sauri. Roderich Kiesewetter da ke zama kwararre kan harkokin waje na kungiyar 'yan majalisu ta jam'iyyar CDU, na ganin cewar kasar Jamus hali na cikin tsaka mai wuya. Ya zama wajibi Jamus ta fahimci cewa tsarin mulkin dimukuradiyya da tsarin mulkin shi kansa na kara fuskantar barazana. Alal misali, a halin yanzu kasar Chaina tana yin duk abin da za ta iya don fadada tasirinta, da kuma kara dogaro da kasashen dimukuradiyya kamar Jamus ke yi da ita.
Ko da idan aka zo ga batun da ya ke daukar hankali a halin yanzu na manufofin Ukraine, babu abin da zai ci gaba da kasancewa kamar a da. Bayan yakin Rasha da Ukraine tun daga bazarar 2022, Jamus ita ce babbar mai goyon bayan Ukraine bayan Amurka, ta hanyar soja da kuma ta fuskar daukar 'yan gudun hijira.
Talla
Sojojin zaman lafiya na Jamus a Ukraine?
Farin jinin shugaban gwamnatin Jamus Olaf Scholz ya ragi idan aka kwatanta da zaben da ya gabata.Hoto: Kay Nietfeld/dpa-Pool/picture alliance
Shugaban gwamnati na yanzu Olaf Scholz ya ce da kamar wuya a iya aiwatar da shi a zahiri, inda ya ce: "Dole ne mu ci gaba da tallafa wa Yukraine, dole ne kuma ta samu tabbacin dogaro da mu na cewa hakan zai kasance. Muna maraba da cewar, ana tattaunawa kan batun zaman lafiya. Amma dole ne mus an halin da ake ciki game da wannan yunkuri, kuma dole a yi la'akari da matayin Ukraine na yarda da abin da aka gabatar mata."
Yanzu akwai barazanar yiwuwar cimma yarjejeniyar kawo karshen yakin Ukraine, wanda mai yiwuwa Amurka da Rasha ne kawai za su yi tattauna. Jamus da sauran kasashen Turai, su ne ke da alhakin tabbatar da aiwatar da yarjejeniyar da sojojinsu. Ko ta ya ya dai, shugaban Amurka Donald Trump ya riga ya bayyana cewa, wajibi ne a kawo karshen yakin.
Gabannin babban zaben Jamus da ke tafe a watan Fabarairu, jam'iyyun siyasar kasar sun tsayar da 'yan takarar su.
Hoto: Carsten Koall/dpa/picture alliance
Olaf Scholz, jam'iyyar SPD (An haife shi a shekarar 1958)
Dan jam'iyyar Social Democrats wanda ke da kamfanin lauyoyi, ya shafe shekaru ana gwagwarmayar siyasar Jamus da shi, ya rike mukaman gwamnati kama daga magajin garin birnin Hamburg da ministan kwadago da ministan kudi da ma shugaban gwamnati. Olaf Scholz ya kasa daukaka kimarsa ta yadda zai kara samun kwajini a tsakanin al'umma.
Hoto: Carsten Koall/dpa/picture alliance
Friedrich Merz, jam'iyyar CDU (An haife shi a sheklarar 1955)
Mai ra'ayin yan mazan jiya, Friedrich Merz dan takarar neman kujerar shugaban gwamnati mafi tsufa da Jamus ke gani a sama da shekaru 50, Merz Lawyan dan kasuwa ne kuma mai bin darikar Katolika da ya fito daga yankin yammacin Jamus bai taba rike mukamin gwamnati ba, sai dai yana da gogewa a fannin kasuwanci tare da kasancewa daya daga cikin manyan kamfanonin kadarori na duniya BlackRock.
Hoto: Ruffer/Caro/picture alliance
Robert Habeck, jam'iyyar Greens (An haife shi a shekarar 1969)
Robert Habeck da ake wa kallon mai saukin kai, dan siyasar da ba shi da matsala wajen amsa kuskurensa, Habeck ne ya samo kalamai masu sauki da ratsa zuciya don bayyana hukunce-hukuncen siyasa na gwamnati ga jama'a tare da kawar da girman kan abokan kawancensa. Kafin shigar sa siyasa, Habeck marubuci ne, mai fassara kuma masanin falsafa.
Hoto: appeler/dpa/picture alliance
Alice Weidel, jam'iyyar AfD (An haife ta a shekarar 1979)
Alice Weidel mataimakiyar shugaban jam'iyyar masu kyamar baki, mai ra'ayin 'yan mazan jiya tana da digirin digirgir a fannin tattalin arziki, ta yi karatu da aiki a kasar China. Weidel na da tsatsauran ra'ayi a kan bakin haure. Yanzu haka tana rayuwa da wata mace kawarta 'yar asalin Sri Lanka a kasar Switzerland inda suke da 'ya'yan riko biyu.
Christian Lindner, Jam'iyyar FDP (An haife shi a shekarar 1979)
Tsohon ministan kudi wanda masanin kimiyar siyasa ne, Christain Lindner ya samar da kamfanin yin sana'ar talla kazalika jami'in sojin ajiya ne a rundunar sojin saman Jamus. Ya zama shugaban jam'iyyarsa ta Free Democrats tun yana da shekaru 34 kacal kuma ya ci gaba da zama shugaba ba tare da wata hammaya ba. Lindner ya lakanci kafofin sadarwar zamani kuma yana matukar sha'awar motocin wasanni.
Hoto: Hannes P Albert/dpa/picture alliance
Sahra Wagenknecht, jam'iyyar BSW (An haife ta a shekarar 1969)
Sahra Wagenknecht jigo ce a jam'iyyar 'yan gaba dai gaba dai, tana yawan ziyarar shirye-shiryen siyasa a kafofin talabijin. Ta yi suna wajen yi wa 'yan siyasa dariya da ma kiransu masu fuska biyu musamman masu ra'ayin mazan jiya da masu kyamar baki. Wagenknecht na da shakka a kan sauyin yanayi da ma sukar kungiyar tsaro ta NATO.
Hoto: Kay Nietfeld/dpa/picture alliance
Jan van Aken, jam'iyyar yan gaba dai-gaba dai (An haife shi a shekarar 1961)
Jan van Aken haifafen Jamus Ta Yamma, yana da digirin digirgir a fannin ilimin halitta, ya kuma yi aiki a matsayin mai binciken makamai a Majalisar Dinkin Duniya. Ya yi zaman majalisa daga jam'iyyar 'yan gaba dai-gaba dai a majalisar dokoki ta Bundestag daga shekarar 2009 zuwa 2017. Tun a watan Oktoban 2024 ya kasance mataimakin shugaban jam'iyyarsa.