Sakamakon zaɓen shugaban ƙasar DRC
November 15, 2006Hukumar zaɓe mai zaman kanta, a Jamahuriya Demokaradiyar kongo, ta kammala tattara sakamakon zaɓen shugaban ƙasa zagaye na 2.
Cibiyoyin ƙidayar ƙuri´u 169, a fadin ƙasar baki ɗaya sun bada sakamakon su.
Shugaban ƙasa mai ci yanzu, Joseph kabila, ya sa mu kashi 58, bisa 100 ,na jimilar ƙuri´un da ka kaɗa, a yayin da abokin hamayar sa, Jean Pierre Bemba, ya tashi da kashi 42 bisa 100.
Kimanin kashi 65 bisa ɗari na al´ummar da ya cencenta su yi zaɓe su ka kaɗa ƙuri´un su.
A yayin da yake bayyana sakamakon, shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta, Apolinaire Malu-Malu ya yi kira ga yan siyasa.
Shima shugaban ƙasa, da ya lashe zaɓen ya yi kiran jama´a ta kwantar da hankulla, to saidai a halin da ake ciki ƙasar na shirin faɗawa cikin wani saban rikici, domin Jean Pierre Bemba, ya ƙi amincewa da sakamakon zaɓen, wanda ya ce an tabka maguɗi a cikin sa.