Karfafa dangantakar Iran da Saudiyya
April 28, 2023![Saudiyya | Bin Faisal | Dangantaka | Iran | Hossein Amir-Abdollahian](https://static.dw.com/image/65244099_800.webp)
Talla
Ministan harkokin kasashen waje na Iran din Hossein Amirabdollahianya bayyana hakan ne a wani taron manema labarai da ya ngudanar a birnin Berut fadar gwamnatin Lebanon, yayin ziyarar aiki da yake a yanzu haka a kasar. Sai dai kuma, Amirabdollahian bai bayar da takamaimiyar ranar da kasashen biyu za su yi bikin sake bude ofisoshin jakadancin nasu ba. A baya dai Tehran da Riyadh na yi wa juna kallon hadarin kaji, kafin a watan Marsi din da ya gabata su amince da farfado da dangantakar da ke tsakaninsu.