Saudiyya ta takaita yawan mahajjata a bana
June 12, 2021![Weltspiegel 10.05.2021 | Corona | Saudi-Arabien Mekka | Gebet mit Abstand](https://static.dw.com/image/57481884_800.webp)
Talla
Sanarwar da masarautar ta fitar a yau Asabar, na cewa masu shekaru 18 zuwa 65 wadadna suka yi rigakafi ne kadai za su samu damar aikin hajjin bana.
Wannan matakin dai na zuwa ne bayan da Saudiyyar ta takaita adadin mahajjata a shekarar 2020, dama dai akalla musulmai miliyan biyu ne ke zuwa sauke faralin aikin hajji a Sadiyya duk shekara.