Ko hakkin dan Adam zai samu kariya?
December 10, 2025
Wannan batu na kare hakin dan Adam batu ne da a kullum kowa ke yi, amma kuma akasari wajen aiwatarwa ana shan bam-bam. A wata hira da ya yi da DW, Malami a jami'ar birnin Tahoua Dakta Atto Namaiwa na ganin cewa, lallai wasu lokutan ana samu kura-kurai wajen kare hakkin dan Adam din da ya kamata a gayara.
Rana mai muhimmanci
Wannan rana ta tunawa da kare hakkin dan Adam, wata dama ce ta nunawa a fili cewa kowa na da alaka da kare hakkin dan Adam da ke zaman tamkar tsara rayuwar al'umma ta yau da kullum.
A wannan lokaci na tashin hankali da rashin tabbas da mutane da yawa ke jin karuwar rashin tsaro, da rashin yarda da kuma kawar da kai kan wasu abubuwan da ya kamata a duba.
'Yancin dan Adam a Nijar
Taken ranar kare hakkin dan Adam din ta bana, na nufin sake tabbatar da kimar 'yancin dan Adam da kuma nuna cewa sun kasance masu karfi ga dan Adam. A bangaren gwamnatin Nijar ofishin ministan shari'a musamman sashen daraktan mai kula da kare hakin dan Adam, sun dukufa wajen ganin an bayar da karfi a fannin hadin kan al'umma da cudanya da juna cikin mutuntawa.