Shugaba Erdogan ya soki lamirin hatta kasar Somaliland
December 30, 2025
Shugaba Recep Tayyip Erdogan na Turkiyya, ya bayyana cewa amincewar da Isra’ila ta yi wa yankin Somaliland a matsayin kasa mai cikakken 'yanci ko kadan bai dace da ka'ida ba, kana ya yi kira ga kasashen duniya da su yi watsi da shi da matakin.
Somaliya ta yi martani kan matsayar Isra'ila kan yankin Somaliland
Shugaban na Turkiyya ya bayyana hakane a yayin da yake karbar bakwancin takwaransa na kasar Somaliya wanda ke ziyarar aiki a birnin Istanbul.
Shugaba Erdogan ya ce, "Daukar matakin kare cikakken 'yancin Somaliya ta kowane hali na da matukar muhimmanci a gare mu. saboda haka, matakin da Isra’ila ta dauka na amincewa da Somaliland ba halattacce ba ne, kuma ba za a yarda da shi ba". a yayin da yake jawabi a gaban manema labarai.
Afirka ta soki na'am da Isra'ila ta yi da Somaliland
Yankin na Somaliland da ke fafutikar ballewa daga Somaliya, ya ayyana kansa a matsayin kasa mai cin gashin kanta tun shekarar 1991 bayan barkewar wani wani mummunan rikici da ya kai ga darewar 'yan kasar gida biyu.