1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Jamus: Aniyar shugaba Steinmeier ta karin wa'adin mulki

Abdoulaye Mamane Amadou
May 28, 2021

Shugaba Frank-Walter Steinmeier na Jamus ya bayyana aniyarsa ta son samun karin wa'adi na biyu na mulkin kasar don taimakawa Jamusawa.

Bundespräsident Frank-Walter Steinmeier
Hoto: Bernd von Jutrczenka/dpa/picture alliance

Dan jam'iyyar SPD da ke cikin kawancen jam'iyyun da ke mulkin Jamus, Steinmeier ya bayyana fatansa na ci gaba da bada tasa gudunmawa wajen sake inganta makomar Jamus da tallafawa mutanen da annobar corona ta yi wa illa sake murmurewa a rayuwa.

Duk da yake jam'iyyarsa ta SPD ta samu koma baya, shugaban da ke kan karagar mulki tun a shekarar 2017 ka iya samun nasarar lashe wani wa'adin mulki idan har ya samu goyon bayan majalisun dokokin kasar biyu na Bundestag da Bundesrat.