1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

Shugaban Askarawan Libiya ya yi marabus

June 9, 2013

Yussef Al Mangush ya ajiye aikin ne, kwana ɗaya bayan zanga zangar da aka yi a birnin Benghazi, wadda a ciki mutane 31 suka mutu.

epa03737886 (FILE) A file photo dated 03 March 2013 shows Libyan Chief of Staff of the Libyan Armed forces, Yussef al-Manqush speaking at a press conference in Tripoli, Libya. Al-Manqush resigned on 09 June 2013 after 31 people were killed in clashes between a militia group and protesters in the eastern city of Benghazi. The country's parliament, the National Congress, approved the resignation of al-Manqush at its evening session. Thirty-one people were killed and dozens injured after protesters gathered outside one of the Libya Shield Brigade offices demanding that it hand over its weapons and be disbanded. EPA/SABRI ELMHEDWI +++(c) dpa - Bildfunk+++
Hoto: picture-alliance/dpa

Majiyoyin gwamnati a ƙasar ta Libiya sun ce Al Mangush ya miƙa takardarsa ta marabus ga Majalisar Dokokin wace tuni ta amince da buƙatar.

Shekaru biyu dai bayan mutuwar kanal Gaddafi tsohon shugaban na Libiya har yanzu gwamnatin ta gaza aiwatar da shirin kwance ɗamarar tsofin mayaƙan 'yan tawayen abin da ke zaman babban cikas ga sha'anin tsaro. Masu aiko da rahotannin sun ce babban jami'in sojin na nuna rashin amincewar sa da tsarin aikin kula da harkokin tsaro da hukumomin suka ƙaddamar tun lokacin da suka karɓi ragamar mulki. A jiya ne dai wasu ɗarurruwan matasan suka gudanar da zanga zanga a birnin Benghazi da zumar neman a kwance ɗamarar tsofin mayaƙan.

Mawallafi : Abdourahamane Hassane

Edita : Saleh Umar Saleh