1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW
SiyasaAsiya

Shugaban Myanmar yana Thailand

Suleiman Babayo AMA
April 4, 2025

Shugaban gwamnatin mulkin sojan Myanmar ya isa kasar Thailand inda ake taron kasashen yankin, bayan kasar ta Myanmar ya fuskanci girgizar kasa da ta halaka dubban mutane cikin kwanakin da suka gabata.

Myanmar Naypyidaw 2025 | Min Aung Hlaing
Janar Min Aung Hlaing shugaban gwamnatin mulkin sojan MyanmarHoto: The Myanmar Military True News Information Team/AP/picture alliance

Shugaban gwamnatin mulkin sojan kasra Myanmar, Janar Min Aung Hlaing ya isa kasar Thailand domin halartar taron kungiyar kasashen yankin, kwanaki bayan girgizar kasar da ta halaka dubban mutane a kasar ta Myanmar. Ba kasafai shugaban gwamnatin mulkin sojan yake tafiya zuwa kasashen ketere ba.

Karin Bayani: Girgizar kasa a Myanmar da Thailand

Galibin kasashen Duniya sun ba sa da wata alaka da gwamnatin mulkin sojan ta Myanmar da Janar Min Aung Hlaing yake jagoranta, tun bayan kifar da gwamnatin farar hula da Aung San Suu Kyi suke take shugabanta a shekara ta 2021.